Majalisar Tarayya za ta binciki harkallar saida tikitin jirgin ƙasa na Kaduna-Abuja da ya kazanta yanzu.
An maida siyan tikitin jirgin kasan Kaduna-Abuja ta hanyar yanar gizo domin a tsaftace harkar sannan don akau da masu harkallar tikitin suna siyar wa matafiya da dan karan tsada.
Wanda ya kashe dan shekara shida a Kaduna ba ma’aikaci ba ne – Rundunar Sojin Najeriya
Tun a watan Janairu ne hukumar Jiragen Kasa ta Kasa NRC ta maida siyan tikitin jirgin kasa na Kaduna zuwa Abuja ta yanar gizo maimakon layi da ake bi a siya a tashar jirgin dake Abuja da Kaduna.
Dan Majalisa Zayyad Ibrahim ne ya ya jagoranci mahawarar a zauren majalisar.
Yace maimakon a samu sauki wahala mutane suka fada ciki tsindum.
” Da farko dai ba a iya siyan tikitin ta yanar gizo, ko shafin ta ki budewa ko kuma ya bude ka iske duk an siye kujerun jirgin.
Zayyad ya ce abin dai ya koma kamar a da, harkalla ma’aikatan suke yi. idan suka siya tikitin sai su rika siyar wa da dan karan tsada a tashar jirgin idan matafiya sun zo.
Gwamnonin Bauchi da Jigawa sun yi kururuwar bayyanar Boko Haram a jihohin su
Abin ya kazanta ta yadda maimakon a samu sauki sai tsananin wuya aka jefa matafiya aka yi.
Idan ba a manta ba makasudin kirkiro siyar da tikitin jirgin ta yanar gizo shine don a dakile harkallar ma’aikatan hukumar da ke nunka kudin tikitin suna saida wa a tashan jirgi wa matafiya.
Majalisar ta amince a gayyato duka jami’an kamfanonin da aka baiwa ikon siyar da tikitin da kuma jami’an hukumar jiragen kasa ta kasa domin su zu su yi bayani a gabanta, sannan su wanke kansu.

SHARE TO FRIENDS
FOLLOW US ON SOCIAL MEDIA FOR LATEST UPDATES
FOLLOW US ON TWITTERLIKE US ON FACEBOOK PAGE
JOIN OUR FACEBOOK GROUP
JOIN OUR WHATSAPP GROUP